SABON BOKA MAI KUNKURU
Da alama Ya Fara Jin Wa'azi Boka Mai Kunkuru Ya Shiryu .
Bokan da Muka Baku Labarin sa Shekarar Data Gabata Harma Muka Saka Maku Lambar Wayarsa domin Wa'azantar Dashi yanzu Da'alama Ya Zama Ustazu...
Gadai Labarin Da Muka Baku Kamar Haka Idan Baku Manta Ba....
Ramatu wata Yarinyace Data Hadu Da sharrin bokaye Kuma Bokancin Yayi Tasiri akanta Wannan labari Ya Faru A Garin LOKON Jihar nasarawa.
Akwai Wani malami Mai suna malam Sani Yana Hada Aikin tsubbace tsubbacensa ne Da Kunkuru Wato Idan Harka Bata Masa rai Da zarar Ya Dakko Kunkurun Ya Rubuta Sunanka a takarda ya dora kunkurun akai Saidai Kawai Kaji Ka fadi Ka
lankwashe Kana Shure shure Idan Kuma Yaga Dama Idan Ya sake Dakko Wannan Kunkurun Ya Sakashi akan Wannan takardar sai kawai kaji Ka tashi
A Shekaranjiya wata yarinya mai suna Ramatu ta zagi Wannan malami wato malam sani arashin sani tace masa boka Shine Shi kuma bai Bata Lokaci ba Wajen yi Mata sihirinsa Kuma ikon alla Yasa sihirin nasa Yayi tasiri akanta inda Yanzu Wannan Abu ya Faru da ramatu harsaida Jama'a suka Bashi Hakuri Kafin Ya Karya Wannan Sihirin Wakilin mikiya Sa'adu Ibrahim Ya Tabbatar Mana Da Faruwar abin inda aka warware sihirin a idonsa Kamar yadda kuke ganin Ajikin Wannan hoton
Ana Da Bukatar malaman addini su Rinka Shiga Sako Da lungu domin Yima Irin Wa yannan Mutanan wa'azi Ko Allah zaisa su rabauta Allah ya tsare mana imaninmu Ameen Idan akwai mai Sha'awar wa'azantar da shi ga lamba wayarsa nan Koda Dai bai Bamu Damar A Saka Lambarsa ba amma Dai wata Kila Ana Iya Samun Wanda Zai Masa Wa'azi Kuma Ya Rabauta....
08035069270
Yanzu Wannan Boka Yace A shirye Yake Ya Daina Abinda Yake Na Tsubbace Tsubbace Nan da wata Daya Sakamakon Wata Yarinya Mai Suna Hadiza Datake Masa Wa'azi A Kullum Wanda Ita Hadizan Ta Hadu Dashi A sakamakon Sanarwar Da Mukayi..

No comments